fidelitybank

Babu wanda yake ingiza mu daga wajeu farwa Nijar – ECOWAS

Date:

Ƙungiyar Raya Tattalin Arziƙin Afirka ta Yamma (Ecowas), ta yi watsi da zarge-zargen cewa, wasu ne daga ƙasashen waje ke ingiza ta a kan lallai sai ta tilasta wa sojojin Nijar, mayar da ƙasar kan tafarkin tsarin mulki.

“Ecowas, ƙungiyar ƙasashe ce mai aiki da dokoki da tsare-tsare, ƙa’idoji da ladubban da suka kafa ta.

Muradinmu shi ne mu kare haƙƙoƙin al’ummarmu,” Omar Touray, shugaban hukumar Ecowas ya ce a lokacin wani jawabi da ya gabatar a Abuja, babban birnin Najeriya.

Omar Touray ya ƙara da cewa Ecowas ba ta ƙaddamar da yaƙi a kan al’ummar Nijar ba, yayin da ake fuskantar barazana kan yiwuwar amfani da ƙrfin soji da nufin mayar da shugaban ƙasar wanda aka zaɓa a kan tafarkin dimokraɗiyya.

Ya ƙara da cewa ƙungiyar ba ta da niyyar mayar da Nijar, ƙasar da za a ruguza. “Ecowas ba za ta taɓa barin al’ummar Nijar su sha wahala a hannun maƙiya a cikin gida da kuma ƙetare ba.

Kawai dai Ecowas ta damu ne da abin da zai kyautata rayuwar al’ummar Nijar.”

Omar Touray ya ce Ecowas za ta yi amfani da “duk wata dama da take da ita” don mayar da zaman doka a ƙasar.

Ya ƙara da cewa sojojin da suka yi juyin mulki a watan Yuli tun farko “sun bijire wa duk wani ƙoƙarinmu na diflomasiyya” kuma ya ce “ba za a taɓa amincewa da” mulkin riƙon ƙwarya tsawon shekara uku da sojojin juyin mulkin suka sanar ba.

www.najnew

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp