fidelitybank

Babu wanda ya tuntube mu akan shiga jam’iyyar APC – NNPP

Date:

Jam’iyyar hamayya ta NNPP a Kano ta ce, kawo yanzu babu wanda ya tuntubeta game da shiga jam’iyyar APC.

Sanusi Bature Dawakin Tofa mai magana da yawun gwamna Abba Kabir Yusuf, ya shaidawa BBC cewa wannan kira da shugaban APC ya yi musu a kwararo suka ji shi.

”Mun ji bayyanin cewa ya miko wannan Æ™oÆ™on bara na gwamna ya dawo jam’iyyar APC to amma abin mamaki shi ne, shi Ganduje a matsayinsa na tsohon gwamna da tsohon mataimakin gwamna ya fi kowa sanin hanyar da ake isarwa gwamna mai ci sako idan ana son ya je wurinsa”, in ji Sanusi.

Ya kuma kara cewa gwamna Yusuf ba shi da wata matsaya ta barin jam’iyyarsa ko kin barin jam’iyyarsa.

”Amma maganar da muka ji ya faÉ—a a kafafen yaÉ—a labarai na zumunta mu ka ji ta kuma a nan mu ka barta’’

”Ka san ita siyasa ko in ce sauya sheka ta siyasa kamar canza gida ne, ba ka tashi lokaci É—aya kawai ka dauki jakarka ka fita, ka ce wai ka canja gida.

“Akwai abubuwan da za ka iya yi kafin ka ce ka canja gida saboda don haka mu a wurinmu wannan sako mun ji ne kawai kamar a sama”, in ji shi.

Wannan yunkuri na jam’iyyar APC na zuwa ne bayan umarni da shugaba Tinubu ya bayar, na cewa É“angarorin biyu su je su sasanta da juna.

Wasu dai na ganin cewa abu ne mai matuƙar wuya waɗannan ɓangarori su iya ajiye rigingimun da ke tsakaninsu su yi aiki tare idan ta tabbata cewa za su haɗe, musamman kan wanda zai zama jagora.

latest news in nigeria 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar Æ´an Æ™asarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp