fidelitybank

Babu wanda ya isa ya sauke ni daga muƙami na – Ayu

Date:

Shugaban babbar jam’iyyar hamayya ta PDP, Dakta Iyorchia Ayu, ya jaddada matsayinsa na shugaban jam’iyyar tare da cewa, babu wanda ya isa ya sauke shi daga muƙaminsa.

Mista Iyorchia Ayu ya yi wannan iƙirarin ne a lokacin da yake ganawa da al’umar ƙabilar Jemgba a gidansa da ke Karamar Hukumar Gboko a jihar Benue da ke arewa ta tsakiyar Najeriya.

Shugaban Jam’iyyar dai na takun saka da wasu gwamnonin jam’iyyarsa ciki har da gwamnan jiharsa ta Benue Samuel Ortom, wanda ke ta kiraye-kirayen ya sauka daga muƙaminsa.

Ya ƙara tabbatar wa mutanen cewa babu abin da zai sa ya sauka daga mukaminsa .

“Jam’iyyar PDP guda ɗaya ce. Ina bakin ƙoƙari na wajen ganin ban ɓata wa al’umar Benue da na Najeriya ba. Dan haka idan kun ji suna ta kiraye-kirayen saukeni daga muƙamina, to kar hakan ya dame ku, babu wanda ya isa ya saukeni daga kan kujerar shugabancin jam’iyyarmu. Kawai zan bar kujerar ne ranar da Allah ya kaddara saukata”, in ji Iyorchia Ayu

nigeria newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

QPC ta nemi INEC ta soke zaɓen Kano

Jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya ta nemi hukumar zaɓe...

Zaɓen Kano: An kama Mutane 288 da tayar da zaune tsaye

Rudunar ƴansandan jihar Kano, ta sanar da kama mutum...

An Kama wakilin jam’iyya da Naira miliyan 25.9 na Siyan Kuri’a

Jami’an tsaro sun kama wani da ake zargin wakilin...

Farashin kayan abinci na rugu-rugu a Najeriya – NBS

Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa (NBS) ta ce hauhawar farashin...

Kotun Kano ta ce a kamo mata Dagacin Tamburawa

Kotun Shari’ar Musulunci da ke shelkwatar Hisbah a Kano,...

Kotu ta ƙwace motocin gwamnatin Zamfara guda 40 daga hannun Matawalle

Kotun Daukaka Kara da ke a Sokoto ta tabbatar...

A na cigaba da gudanar da zaben cike gurbi harda Kano

Kano na ɗaya daga cikin jhihohin da ake kaɗa...

Mutane 12 sun mutu a wani hatsari a Kano – FRSC

Hukumar Kiyaye Haddura ta Ƙasa (FRSC) reshen Kano, ta...

Masarutar Rano ta haramta aurar da Yaran da ba su kammala karatun Firamare ba

Masarautar Rano a Kano ta haramta cire yarinya daga...

Matatar Dangote za ta fara jigilar mai kyauta ga gidajen mai

Matatar man Dangote za ta fara jigilar mai kyauta...

An sassata rikicin da aka shafe shekaru 30 kan Masallacin Sharada da Islamiyya

Tsohon dan takarar gwamnan Kano, Malam Sha’aban Ibrahim Sharada,...

Duk da kalubalen ‘yan siyasa a Kano mun shirya a zaben cike gurbi – INEC

Kwamishinan hukumar zaɓe mai zaman kanta (INEC) reshen jihar...
X whatsapp