fidelitybank

Babu wanda ya isa ya kore ni daga PDP – Wike

Date:

Ministan Abuja, Nyesom Wike ya ƙalubalanci jam’iyyarsa ta PDP kan barazanar korarsa, yana mai cewa babu wanda ya isa.

A lokacin wata tattaunawa da ya yi da kafar Talabijin Channels, ministan ya ce, ba ya tsoron kowa kuma abin da ya ke yi babu batun saɓa ƙa’idar jam’iyya ko kuma zagon-ƙasa.

Wike wanda tsohon gwamnan Ribas ne, ya ce shi dai a iya saninsa bai ga wani shugaba a PDP da ya ke da ikon iya korarsa ba, ko yi masa barazana.

Ministan ya kuma jadadda cewa shi shugaba Tinubu ya ke yiwa aiki, ba wai APC ba don haka babu wanda ya ke bin sa bashi ko ya wajaba ya nemi afuwa daga gareshi.

Sabon ministan na Abuja ya kuma shaida cewa nan da watanni takwas za a ga canji sosai a birni, saboda jirgin ƙasan da zai ke yawo a cikin gari zai soma aiki, sannan mulkinsa zai dawo da abubuwa sosai musamman ainihin tsarin Abuja.

Yana mai shaida cewa dama masu arzikin Abuja ke karya dokoki birnin, don haka za su ɗau duk wani mataki na laɗabtarwa da tabbatar da cewa doka ta yi aiki a kan kowa.

sani ahmad

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp