Peter Obi, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour a zaben 25 ga Fabrairu, 2023, ya dage cewa babu wanda zai iya tilasta masa ficewa daga Najeriya.
Tun da farko Mista Obi ya yi ikirarin cewa yana fuskantar matsin lamba na barin kasar amma ya bayyana cewa ya kuduri aniyar samar da sabuwar Najeriya.
Da yake jawabi a garin Onitsha na jihar Anambra yayin wani gangamin yakin neman zabe na neman goyon bayan Afam Ogene dan takarar jam’iyyar Labour a mazabar tarayya ta Ogbaru, Mista Obi ya bayyana cewa akwai barayi da yawa a kasar nan da ke addabar talakawa.
Karanta Wannan: Fani-Kayode ya caccaki Peter Obi bayan an kama shi a Birtaniya
Sai dai ya jaddada cewa jam’iyyar Labour ta kuduri aniyar kawar da tsarin siyasar kasar daga irin wadannan mutane.
“Don haka, jam’iyyar Labour tana fafutukar samar da sabuwar Najeriya. Ina nan tare da ku, kuma babu wanda zai tilasta ni in bar Najeriya,” in ji Obi.