Tsohon gwamnan jihar Legas, Sanata Bola Ahmed Tinubu, ya ce, ya shirya tunkarar dukannin kowane dan takara da yake shirin tsayawa a 2023.
Tinubu ya bayyana hakan ne a ziyarar da ya kaiwa masu martaba Alaafin na Oyo, Oba Lamidi Adeyemi da kuma zababben Olubadan, Oba Lekan Balogun. a ranar Lahadi, ya sanar da cewa, babu wata barazana da za ta hana shi cimma burinsa a 2023.
Ya ce, ya kai ziyarar ne ga iyayen gargajiyan, domin su saka masa albarka, su bashi hadin kai, kuma su yi masa addu’ar hayewa shugabancin kasa a 2023.
A yayin jawabi a fadar zababben Olubadan da ke Ibadan, jigon jam’iyya mai mulkin ya ce, babu irin barazanar da za ta hana shi cika burinsa.