fidelitybank

Babu gudu ba ja da baya a kan goyon bayan mu ga Fubara – Gwamnonin PDP

Date:

Gwamnonin da aka zaba a karkashin jam’iyyar PDP, sun dage cewa sun amince da Gwamna Siminalayi Fubara na jihar Ribas a matsayin shugaban jam’iyyar a jihar.

Tsohon gwamnan jihar, Nyesom Wike da Fubara sun yi ta gwabzawa da tsarin shugabancin jam’iyyar.

Wike, ministan babban birnin tarayya Abuja a halin yanzu, ya gargadi gwamnonin PDP da su kaurace wa jihar Ribas, inda ya yi barazanar cewa zai cinna wuta a jihohinsu daban-daban idan suka ci gaba da marawa godson sa baya.

Sai dai kuma da yake mayar da martani kan ficewar Wike, shugaban kungiyar gwamnonin PDP, Gwamna Bala Mohammed ya ce, babu gudu babu ja da baya kan goyon bayan su ga Fubara.

Da yake jawabi a lokacin da ya karbi tawagar kwamitin gudanarwa na jam’iyyar na kasa, NWC, Mohammed, gwamnan jihar Bauchi mai ci ya ce matakin da gwamnonin PDP suka dauka yana nan daram.

Da yake yiwa manema labarai jawabi jim kadan bayan taron, Mohammed ya kara da cewa a matsayinsa na daya daga cikin ‘yan jam’iyyar PDP a jihar Ribas, ya kamata a bar Gwamna Fubara ya mallaki tsarin jam’iyyar.

Ya shaida wa manema labarai cewa tawagar NWC ta goyi bayan “hukuncin da kungiyar gwamnonin PDP ta dauka na marawa gwamnan jihar Ribas Similaye Fubara a matsayin shugaban jam’iyyar PDP a jihar.

“Shawarar tana cikin tsari kuma haka ya kamata ta kasance. Gwamna Fubara shi ne shugaban jam’iyyar a jihar. A kan haka ne muka amince tare da bin doka da oda, kuma tawagar ta ba da kwarin gwiwa da goyon bayansu ga matsayin kungiyar gwamnonin PDP a jihar Ribas.”

“Dukkanmu mun san alakar da ke tsakanin Ministan babban birnin tarayya da kuma Gwamnan Jihar Ribas na yanzu wanda shi ne na mai ba da shawara da kuma wanda aka yi masa jagora. Muna aiki a bayan fage don ganin sun taru don yin aiki tare kamar yadda aka san PDP.

“Tabbas, ba abu ne da za mu iya fada a nan ba amma mun yi kira da jajircewa da kuma niyya don ganin an yi abin da ya dace,” in ji shi.

www.nigerianews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp