fidelitybank

Babu batun ƙara kuɗin makaranta ga ɗalibai – Gwamnatin Tarayya

Date:

Fadar shugaban kasa, ta ce, babu batun ƙarin kudin karatu (tution fee) a ckin kuɗaɗen da jami’o’in gwamnatin tarayya ta ƙarawa ɗalibai.

Dele Alake, mai ba shugaban kasa shawara kan ayyuka na musamman ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a ranar Laraba.

A baya-bayan nan ne mahukuntan Jami’ar Legas suka ƙara kuɗaɗen makaranta da dalibai za su biya daga N19,000 zuwa N190,250 ga daliban da ke karatun likitanci kuma N140,250 ga daliban da ke karatun sauran kwasa.

Wannan ya haifar da wasu martani yayin da mutane da dama suka soki matakin, wanda ya zo a lokacin da ake fama da raɗaɗin cire tallafin man fetur da shugaba Tinubu yayi.

Sanarwar ta ce “A farkon makon nan ne wasu kafafen yada labarai suka yada labarin cewa Gwamnati ta ƙara kudin karatu a jami’o’in gwamnatin tarayya a kasar nan.”

“Waɗannan rahotannin ba daidai ba ne. Muna sane da cewa wasu jami’o’i a ‘yan makonnin da suka gabata sun sanar da karin kudin da dalibai ke biya na makaranta.”

“Sai dai kuma mun tabbatar da cewa wadannan kudade da jami’o’i suka ƙarawa dalibai na wurin kwanan dalibai ne da sabuwar rijistar da akeyi duk bayan zangon karatu da dakin gwaje-gwaje da sauran kuɗaɗe amma banda kudin karatu (tution fee) a ciki.”

“Mahukuntan wadannan jami’o’in ma sun bayyana wannan hujjar sosai wajen bayyana dalilan da suka sa akayi ƙarin waɗannan kudade don gujewa shakku.”

Sanarwar ta ƙara da cewa shugaba Tinubu ya ci gaba da jajircewa kan alkawarin da ya dauka na ganin kowane dan Najeriya ba tare da la’akari da yanayin tattalin arzikin iyayensa ba, ya samu damar samun ingantaccen ilimi a manyan makarantu.

nigerianews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp