Hukumar shirya jarabawar shiga makarantun gaba da sakandire ta JAMB, ta gargadi jama’a da suka yi jarrabawar gama sakandare ta 2022, da su yi hattara da yaudara da sauran ayyukan da ba su dace ba na ‘yan damfara.
Hukumar ta JAMB ta bayyana haka ne ta bakin shugabanta, hulda da jama’a da kuma tsare-tsare na JAMB, Dr. Fabian Benjamin a Abuja ranar Talata.
Hukumar ta ci gaba da cewa, UTME jarrabawa ce ta kwamfuta wacce aka samu ta hanyar lantarki ba tare da shiga tsakani na dan Adam ba.
A cewar hukumar ta JAMB, jita-jitan da ba su da tushe balle makama da ake ta yadawa ba komai bane illa yaudarar kwakwale na masu shirya wadannan zage-zage marasa tushe.
Ya sake nanata cewa babu inda za a yi kurakurai a tsarin sa na lantarki ko kuma ba ta shirin shirya wani UTME ba