fidelitybank

Babu batun maganar baiwa ASUU Naira dubu 10 – PTA

Date:

Kungiyar iyayen yara da malamai ta ƙasa, ta karyata maganar cewa za ta bayar da gudunmawar Naira 10,000 kowannensu ga kungiyar malaman jami’o’i, ASUU, domin kawo karshen yajin aikin na watanni 6.

A wata sanarwa da shugaban kungiyar na kasa Alhaji Haruna Danjuma ya fitar, ya nesanta kungiyar daga wannan ikirarin.

Ya yi bayanin cewa PTA ba ta da masaniyar wannan furucin, ya kuma gargadi wani ko wasu jama’a da su yi amfani da sunan su wajen kawo rudani a kasar nan.

A cewar sa, “Ba mu da hannu a duk wata sanarwa da ta shafi biyan kudi ga ASUU domin su janye yajin aikin da suke yi.”

Ya kara da cewa, “A matsayinmu na tun da aka fara yajin aikin, shi ne kungiyar ASUU da gwamnatin tarayya su cimma matsaya, wato a kawo karshen yajin aikin amma ba wai a ba da kudi don biyan ASUU ba.

Yayin da yake kira ga gwamnatin tarayya da ta saurari bukatar ASUU, shugaban PTA ya kuma roki gwamnatin tarayya da ta kubutar da duk daliban makarantar sakandare da aka yi garkuwa da su da sauran ‘yan Najeriya a fadin kasar nan da ke hannun ‘yan bindiga.

Danjuma ya koka kan halin da ake ciki a Yawuri, inda har yanzu dalibai mata da aka sace suna hannun ‘yan bindiga sama da kwanaki 400.

legitnews.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An fara binciken fashewar wani abu da ya kashe mutane 5 da jikkata da dama a Kano

Wani abin fashewa da ake tunanin bom ne ya...

An samu fashewar wani abu a kamfanin ƴan Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...

Kotu ta ɗaure Matashin da yake tare titi a Kano da sunan barƙwanci

Kotun majistire da ke unguwar Nomansland a Kano, karkashin...

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...
X whatsapp