fidelitybank

Babu batun hadewa tsakanin Kwankwaso da Obi – Buba Galadima

Date:

Jigo a jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP), Buba Galadima ya karyata labarin da ke cewa, dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar, Rabiu Kwankwaso da Peter Obi, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour Party (LP) na shirin hadewa kafin nan da zaben shugaban kasa na 2023.

Galadima wanda ya yi magana a shirin talabijin na Arise a ranar Litinin din da ta gabata ya ce sabanin rade-radin mutane, cewa ‘yan takarar shugaban kasa biyu suna tattaunawa ne kan “ kawancen zabe, ba hadewa ba.

Jigo a jam’iyyar NNPP wanda ya ce shi ne ya jagoranci kwamitin sasantawa ya bayyana cewa dukkanin bangarorin biyu suna da fahimtar kusan dukkanin batutuwan da aka tabo sai daya – wato wanda ya kamata ya zama dan takarar shugaban kasa, da kuma wanda ya kamata ya tsaya masa.

Ya ce, “Ba mu tattauna batun hadewa da jam’iyyar Labour ba. Abin da muke tattaunawa akai shi ne kawancen zabe tsakanin dan takarar jam’iyyar New Nigerian Peoples Party da dan takarar jam’iyyar Labour.

“Na jagoranci tattaunawar na tsawon sa’o’i 13 masu kyau kuma muna da fahimtar kusan dukkanin batutuwan da aka gabatar sai daya – wanda ya kamata ya zama dan takarar shugaban kasa, da kuma wanda ya kamata ya tsaya masa.”

Galadima ya kuma bayyana cewa wadanda ke cewa “cin mutunci ne” su nemi Peter Obi ya tsige Kwankwaso “ba ‘yan siyasa ba ne,” domin da su ‘yan siyasa ne, da ma ba su yi mafarkin hakan ba.

Ya kara da cewa yayin da kungiyar Peter Obi ta fara watanni biyu kacal da suka wuce, kungiyar Kwankwaso ta “Kwankwasiyya Movement” ta shafe shekaru 32 tana mulki.

uanguard news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp