fidelitybank

Babu batun hadewa tsakanin Kwankwaso da Obi – Buba Galadima

Date:

Jigo a jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP), Buba Galadima ya karyata labarin da ke cewa, dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar, Rabiu Kwankwaso da Peter Obi, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour Party (LP) na shirin hadewa kafin nan da zaben shugaban kasa na 2023.

Galadima wanda ya yi magana a shirin talabijin na Arise a ranar Litinin din da ta gabata ya ce sabanin rade-radin mutane, cewa ‘yan takarar shugaban kasa biyu suna tattaunawa ne kan “ kawancen zabe, ba hadewa ba.

Jigo a jam’iyyar NNPP wanda ya ce shi ne ya jagoranci kwamitin sasantawa ya bayyana cewa dukkanin bangarorin biyu suna da fahimtar kusan dukkanin batutuwan da aka tabo sai daya – wato wanda ya kamata ya zama dan takarar shugaban kasa, da kuma wanda ya kamata ya tsaya masa.

Ya ce, “Ba mu tattauna batun hadewa da jam’iyyar Labour ba. Abin da muke tattaunawa akai shi ne kawancen zabe tsakanin dan takarar jam’iyyar New Nigerian Peoples Party da dan takarar jam’iyyar Labour.

“Na jagoranci tattaunawar na tsawon sa’o’i 13 masu kyau kuma muna da fahimtar kusan dukkanin batutuwan da aka gabatar sai daya – wanda ya kamata ya zama dan takarar shugaban kasa, da kuma wanda ya kamata ya tsaya masa.”

Galadima ya kuma bayyana cewa wadanda ke cewa “cin mutunci ne” su nemi Peter Obi ya tsige Kwankwaso “ba ‘yan siyasa ba ne,” domin da su ‘yan siyasa ne, da ma ba su yi mafarkin hakan ba.

Ya kara da cewa yayin da kungiyar Peter Obi ta fara watanni biyu kacal da suka wuce, kungiyar Kwankwaso ta “Kwankwasiyya Movement” ta shafe shekaru 32 tana mulki.

general news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ina nan a PDP na ban gudu ba – Adeleke

Gwamnan jihar Osun, ya musanta rahotonnin da ke cewa...

Tinubu ya isa birnin Rio na Brazil don halartar taron BRICS

Shugaban kasa Bola Tinubu ya isa birnin Rio de...

Matakan da muke ɗauka kan kisan matafiya a Plateau – Mutfwang

Gwamna Caleb Mutfwang na jihar Filato, ya ce gwamnatinsa...

Tinubu ya gaji tattalin arziki da ya kusa durkushewa – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyeson Wike, ya ce...

Har yanzu PDP tana nan da ƙarfinta – Isa Ashiru

Yayin da fagen siyasar Najeriya ke ci gaba da...

An kama ɗan shekara 70 kan zargin kashe ƙanwarsa a Jigawa

Rundunar ƴansandan jihar Jigawa da ke arewacin Najeriya ta...

Ahmed Musa za ma sabon shugaban gudanarwar Kano Pillars

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya naɗa kyaftin...

Netherlands da Jamus sun zargi Rasha da aiki da makamai masu guba a Ukraine

Hukumomin leƙen asirin ƙasashen Netherlands da Jamus sun zargi...

Kotu ta bayar da umarni Majalisa ta dawo da Sanata Natasha

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja, ta buƙaci...

Sojoji sun hallaka ƴanbindiga da dama a Plateau

Rundunar sojoji ta ce, ta kashe ƴanbindiga da dama...

Duk wani tuggun ku Atiku da El-Rufa’i ba za ku iya kayar da Tinubu ba – Bwala

Fadar shugaban kasa ta yi watsi da kokarin da...

Mutuwar Dantata ta girgiza kasa baki daya – Tinubu

Shugaban kasa Ahmad Bola Tinubu ya bayyana Alhaji Aminu...
X whatsapp