Tsohon shugaban kasa, Cif Olusegun Obasanjo, ya sake nanata kudurinsa na ficewa daga harkokin siyasar jam’iyyar, inda ya ce babu abin da zai sa ya sake koma siyasar jam’iyya.
Obasanjo ya bayyana hakan ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai jim kadan, bayan wata ganawar sirri da ‘yan kwamitin ayyuka na jam’iyyar PDP na kasa a Abeokuta a ranar Asabar.
Ya ce, ya gamsu da zama dattijo, inda ya kara da cewa, babu abin da zai sa ya koma siyasar jam’iyya.
“Ina so in jaddada cewa, yanzu ba na cikin siyasar bangaranci, kuma babu wani abu da zai dawo da ni siyasar bangaranci.
“Zan kasance mai sha’awar abin da ke da kyau ga Najeriya kuma duk wanda ke son samun shawarata, zan ba shi musamman domin amfanin Najeriya da kuma maslahar Afirka”. In ji Obasanjo.
.