fidelitybank

Babu abin da zai hana a rantsar da Tinubu – Sarkin Musulmai

Date:

Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammadu Sa’ad Abubakar, ya ce babu abin da zai hana a rantsar da zababben shugaban kasa, Bola Tinubu a ranar 29 ga watan Mayu.

Abubakar ya bayyana hakan ne yayin da ya bukaci ‘yan Najeriya da su yi wa gwamnatin Tinubu addu’a domin samun nasara.

Ya yi wannan jawabi ne a wani taron tattaunawa da sarakunan gargajiya da na addini wanda bankin duniya ya shirya ranar Laraba a Abuja.

Karanta Wannan: Osinbajo ya fi Tinubu cancantar mulkar Najeriya – Peter Obi

Ya ce: “Dole ne a samu canji domin nan da ‘yan kwanaki ko makonni masu zuwa za a samu sabuwar gwamnati; me za mu iya ba wa waccan gwamnatin don ta daidaita?

“Ko kowa ya so, dole ne a yi shi, sabuwar gwamnati za ta zo a ranar 29 ga Mayu, don haka me za mu yi banda addu’a, saboda mun yi imani da Allah Madaukakin Sarki, mun yi imani da Allah mai bayarwa da karba.

“Bayan haka me? Me za mu yi don taimakawa gwamnati ta daidaita da ciyar da kasar gaba?

Ya kuma bukaci ‘yan Najeriya da su hada kai su yi aiki domin tabbatar da gaskiya da adalci.

legit latest news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp