fidelitybank

Babbar Magana: ‘Yan Bindiga sun sace tsohon shugaban hukumar yi kasa hidima ta NYSC

Date:

 

Wasu ƴanbindiga ɗauke da muggan makamai sun sace tsohon shugaban Hukumar yi wa Ƙasa Hidima ta Najeriya, NYSC, Manjo Janar Mahrazu Tsiga, mai ritaya.

Kwamishinan tsaro da al’amuran cikin gida na jihar, Dakta Nasiru Mu’azu ya tabbatar wa BBC cewa an sace Manjo Janar Tsiga a garin Tsiga da ke yankin ƙaramar hukumar Kankara ranar Laraba da daddare.

”An sace shi ne tare da wasu mazauna garin 13 ciki har da mata biyu, a lokacin da maharan suka auka wa garin, kodayake daga baya mutum huɗu sun kuɓuto”, kamar yadda ya yi ƙarin haske.

Duk da cewa ƙaramar hukumar Kankara na fama da matsalolin ‘yanbindiga, amma garin Tsiga bai saba fuskantar irin wannan matsala ba.

To amma kwamishinan tsaron ya ce a baya-bayan nan sau uku masu garkuwa da mutane na shiga garin tare da sace mutane.

Kwamishinan tsaron ya kuma yi zargin cewa masu tsegunta wa ‘yanbindiga bayanai ne suka tsegunta musu shigar tsohon Janar ɗin zuwa garin ”saboda a ranar Laraba da rana ne ya shiga garin, kuma da daddare suka je suka ɗauke shi”.

”Daga bayanan da muka samu tsohon janar ɗin bai je garin da rakiyar jami’an tsaro ba, ya je ne da direbansa kawai”, a cewar kwamishinan.

Ya kuma gwamnati ce da jami’an tsaro na ƙoƙari domin tabbatar da ceto mutanen da ‘yanbindigar suka sace.

nnn news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...
X whatsapp