Babban layin wutar lantarki na ƙasa zai ci gaba da fuskantar matsaloli sakamakon gazawar gwamnati wajen gyara wani muhimmin layin lantarki a arewacin Najeriya saboda rashin tsaro da ake fama da shi.
Ministan wutar Lantarki, Adebayo Adelabu ne ya bayyana haka, yayin da ya ke magana a zaman kare kasafin kuɗin 2025 a gaban kwamitin haɗin gwiwa na Majalisar Dattawa kan wutar lantarki.
Adelabu ya bayyana tasirin layin Shiroro-Kaduna-Mando da ya lalace, wanda ba ya aiki tun bayan lalata shi da aka yi a watan Oktoban 2024. Wannan gazawar ta sanya matsin lamba sosai a kan babban layin, wanda ke haifar da faɗuwarsa akai-akai.
Ministan ya jaddada cewa yayin da ake ganin layin lantarkin zai ci gaba da faɗuwa, gwamnati ta mai da hankali kan rage yawan afkuwar hakan.
Ministan ya kuma bayyana shirin amfani da kuɗin da suka kai Naira biliyan 36 wajen rabon taransfoma a ɓangarori daban-daban na ƙasar.