fidelitybank

Babban layin lantarki zai ci gaba da lalacewa – Ministan Lantarki

Date:

Babban layin wutar lantarki na ƙasa zai ci gaba da fuskantar matsaloli sakamakon gazawar gwamnati wajen gyara wani muhimmin layin lantarki a arewacin Najeriya saboda rashin tsaro da ake fama da shi.

Ministan wutar Lantarki, Adebayo Adelabu ne ya bayyana haka, yayin da ya ke magana a zaman kare kasafin kuɗin 2025 a gaban kwamitin haɗin gwiwa na Majalisar Dattawa kan wutar lantarki.

Adelabu ya bayyana tasirin layin Shiroro-Kaduna-Mando da ya lalace, wanda ba ya aiki tun bayan lalata shi da aka yi a watan Oktoban 2024. Wannan gazawar ta sanya matsin lamba sosai a kan babban layin, wanda ke haifar da faɗuwarsa akai-akai.

Ministan ya jaddada cewa yayin da ake ganin layin lantarkin zai ci gaba da faɗuwa, gwamnati ta mai da hankali kan rage yawan afkuwar hakan.

Ministan ya kuma bayyana shirin amfani da kuɗin da suka kai Naira biliyan 36 wajen rabon taransfoma a ɓangarori daban-daban na ƙasar.

naija hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp