Babban layin lantarki na Najeriya ya samu wata matsala, lamarin da ya haifar da ɗaukewa lantarkin a wasu sassan ƙasar.
Cikin wata sanarwa da kamfanin rarraba wutar lantarki na birnin Abuja ya fitar a shafinsa na X, ya ce matsalar ta faru ne da misalin ƙarfe 11:34 na safe.
Sai dai kamfanin ya ce masu ruwa da tsaki na aiki tuƙuru domin maido da wutar da zarar an magance matsalar.
Babban layin lantarki na Najeriyar ya saba samun matsalolin faɗuwa, musamman a shekarar da ta gabata, wani abu da ke haifar da matsalar ɗaukewar wutar a faɗin ƙasar.