Wasu rahotanni na nuni da cewa an jibge jami’an tsaro a kofar fita daga masarautar Kano da ke Kofar Kudu daidai lokacin da Sarki Sanusi ke shirin tafiya garin Bichi don raka sabon Hakimi.
Yayin da wasu rahotonnin da muke samu daga garin Bichin ke cewa, jami’an tsaro sun hana shige da fice a gidan sarautar Bichi.
Kawo yanzu dai ba a san wani dalilin yin hakan ba ga jami’an tsaron, sai dai a nan gaba za mu ji ta bakin su dangane da wannan matakin na garkame fadar masarautar Kano.