Babban hafsan sojin ƙasa na Najeriya laftanal Janar Faruk Yahaya ya kai ziyara inda aka kai wa jirgin ƙasa hari a hanyar Abuja Kaduna a ranar Litinin.
Rundunar sojin Najeriya ta wallafa hotunansa a Facebook tare da tawagarsa ta sojoji a wurin da aka kai harin.
Sanarwar ta ce, ya tafi ne domin diba yanayin wurin da girman harin.
Ya kuma umarci sojoji da su tsawaita bincike domin kuɓutar da mutanen da aka sace.
Bayanai sun nuna cewa kimanin mutum 1000 ne a cikin jirgin, wanda aka kai wa hari ranar Litinin da daddare.
Rahotanni sun ce, an sace mutane da dama sannan an kashe wasu, abin da ya jijjiga iyalai da ‘yan uwan fasinjojin da ke cikin jirgin.