Tsohon gwarzon dan kwallon duniya, Cristiano Ronaldo ya ce, babban burin shi a kwallo shi ne lashe gasar cin kofin duniya tare da tawagar Portugal.
A sakonsa da ya wallafa a shafukan soshiyal midiya, Ronaldo ya ce wannan fatan ya gushe a jiya Asabar bayan an doke su a gasar cin kofin duniya.
Wannan ne karon farko da ya bara tun bayan da Maroko ta samu galaba a kan Portugal a Qatar.
“Na fafata a gasar cin kofin duniya a cikin shekaru 16 tare da manyan ‘yan wasa, kuma ba zan taba kasa a guiwa ba,” in ji Ronaldo.
Ya kara da cewa “Ina godiya ga Portugal da sauran ‘yan wasanmu kuma ba zan taba juya musu baya ba.”