fidelitybank

Babban alkalin jihar Oyo ya kafa kwamiti mutum 7 a kan mataimakin gwamna

Date:

A ranar Alhamis ne babban alkalin jihar Oyo, Munta Abimbola, ya kafa kwamitin mutum bakwai da zai binciki zarge-zargen da majalisar ta yi wa mataimakin gwamnan jihar, Rauf Olaniyan.

Majalisar dai na yunkurin tsige Olaniyan, matakin da ya kara tsananta, bayan da mataimakin gwamnan ya fice daga jam’iyyar Peoples Democratic Party, zuwa jam’iyyar All Progressives Congress.

Gwamnan jihar, Seyi Makinde da mafi yawan ‘yan majalisar jihar suna cikin jam’iyyar PDP.

Olaniyan ya yi zargin cewa, Makinde ya yi watsi da shi tare da mayar da shi bayan gwamnatinsa kafin ya sauya sheka.

Sai dai an kafa kwamitin ne, bisa ga kudurin majalisar, kuma kamar yadda kakakinta Adebo Ogundoyin ya bukata.

Ogundoyin ya yi wannan bukata ne a wata wasika mai kwanan wata 6 ga Yuli, 2022.

Shugaban majalisar a cikin wasikar, ya bukaci kundin tsarin mulkin kwamitin bisa ga ikon da aka bai wa babban alkalin jihar ta sashi na 188 (5) na kundin tsarin mulkin tarayyar Najeriya na shekarar 1999.

Mambobin kwamitin sun hada da Cif Kayode Christopher (Shugaban); Adebisi Soyombo; Cif Lawal Adekunle Dauda; Gimbiya Olanike Olusegun; Rev Fr. Patrick Ademola; Cif Mrs Wuraola Adepoju (JP); da Alh. Tirimisiyu Akewusola Badmus.

national tribune newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kashe mayaƙan Boko Haram Takwas a jihar Borno

Rundunar sojin Najeriya ta ce sojojinta sun kashe aƙalla...

Sauya sunan Kwaleji a Oyo ya fusata Dalibai

Ɗaliban kwalejin fasaha ta Ibadan sun gudanar da zanga-zanga...

Tawagar gwamnatin Kano da Jigawa sun kai ziyarar ta’aziyya ga iyalan Dantata

Tawagar gwamnatin Kano da Jigawa sun kai ziyarar ta'aziyya...

Trump ba shi da hankali ko tunani a kan harajin sa – Elon Musk

Tsohon mai ba shugaban Amurka Donald Trump shawara kan...

Dangote ya rage man fetur lita 840

Matatar man Dangote ta rage farashin litar man fetur...

Wa’adin da Najeriya ta bai wa Facebook na biyan tarar dala miliyan 290 ya cika

A ranar Litinin ne wa'adin da wata kotu ta...

Jami’an sa-kan Zamfara sun kashe Kacalla Ɗanbokolo ubangidan Turji

Gwamnatin jihar Zamfara da ke arewa maso yammcin Najeriya...

PDP ta gudanar da taron ta na kasa

Shugabani da gwamnonin da sauran masu ruwa da tsaki...

An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata zuwa Talata

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

‘Yansanda sun kwace iko da sakatariyar PDP a Abuja

A yayin da ake ci gaba da takun-saka kan...

Iran ta na da ‘yancin yin Nukiliyar ta – Ravanchi

Iran ta dage kan hakkinta na ci gaba da...
X whatsapp