fidelitybank

Ba zan tsoma baki ba a sabuwar hukumar BAROTA – Gwamnan Bauchi

Date:

Gwamnan jihar Bauchi, Bala Abdulkadir Mohammed, ya bada tabbacin cewa gwamnatin sa ba za ta tsoma baki cikin ayyukan hukumar kula da zirga-zirgar ababen hawa ta jihar Bauchi (BAROTA) da aka kafa ba domin tabbatar da gaskiya da kuma kwarewa.

Gwamna Mohammed ya yi wannan alkawarin ne a ranar Asabar din da ta gabata a yayin bikin kaddamar da faretin rukunin farko na Kadet da Marshals na hukumar 500 a dandalin Dr. Rilwanu Sulaiman Adamu da ke gidan gwamnati a Bauchi.

Ya kuma jaddada cewa, samar da hukumar shine don magance matsalolin da suka addabi hanyoyin mota, tsaro, da tabbatar da doka a jihar.

“Kafa BAROTA an yi shi ne saboda bukatar gaggawa na magance matsalolin da suka addabi hanyoyin mota, tsaro, da tabbatar da doka a jihar Bauchi,” in ji Gwamna Mohammed.

“Gwamnatina ta himmatu wajen tabbatar da cewa BAROTA tana gudanar da ayyukanta bisa dogaro da kai, ba tare da tsangwama ba.”

Gwamnan ya bayyana cewa ayyukan hukumar, kamar yadda dokar da ta ba da damar ta zayyana, sun hada da tabbatar da bin doka da oda, rigakafin hadurra, bayar da shawarwari kan kiyaye hanyoyin mota, da kuma ikon kama masu laifi.

Ya jaddada cewa an samar da BAROTA ne domin kare rayukan masu amfani da hanyoyin da kuma tabbatar da tsaro da ingantaccen tsarin sufurin titinan jihar.

Gwamnan ya kara da cewa “A tsawon shekarun da suka gabata, hadurran kan tituna, cunkoson ababen hawa, da kuma rikice-rikicen da ke faruwa a hanyoyinmu sun yi illa ga ‘yan kasar.”

“Saboda haka gwamnatina ta gabatar da kudirin dokar hukumar kula da zirga-zirgar ababen hawa ta Bauchi a gaban majalisar dokokin jihar a shekarar 2020. Bayan da aka amince da shi, BAROTA ta kasance wata hukuma ta doka don kare rayukan masu amfani da hanyoyin a jihar.”

Gwamna Mohammed ya kuma bukaci sabbin horar da ‘yan Kadeta da Marshals da su kasance masu aikin wanzar da zaman lafiya, malamai da masu kare lafiyar jama’a.

“Ina roƙonku da ku yi hidima cikin gaskiya, ƙwarewa, da tausayi. Duk wani rai da aka ceto da duk wani hatsarin da aka kiyaye zai kasance sakamakon sadaukarwa da jajircewarku kai tsaye,” in ji gwamnan.

“Gwamnatinmu ba za ta amince da rashin ladabi, rashin da’a, ko cin zarafin damar da ke da alaƙa da lalata ba.”

today nation

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Najeriya na neman dala biliyan 25 na bututun iskar gas zuwa Turai

Najeriya na neman dala biliyan 25 a matsayin kuɗin...

‘Yan sa-kai biyu ne suka mutu a harin da muka kai Zamfara – Sojoji

Rundunar sojin sama ta Najeirya ta tabbatar da kai...

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...
X whatsapp