fidelitybank

Ba zan taba barin ASUU ta tafi Yajin aiki ba – Atiku

Date:

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya ce kungiyar malaman jami’o’i, ASUU, ba za ta shiga yajin aiki ba idan aka zabe shi a matsayin shugaban kasa.

Atiku ya ce, gazawar gwamnati na warware yajin aikin ASUU ba zai taba faruwa a karkashin gwamnatin sa ba.

Ya yi wannan jawabi ne a wajen taron tunawa da ranar matasa ta duniya na shekarar 2022 a Abuja ranar Juma’a.

Atiku ya jadadda cewa mafi muhimmanci kuma hakki na kowane matashi shi ne ‘yancin neman ilimi.

Ya ce: “Saboda haka, na yi watsi da yajin aikin ASUU. Rashin iyawar gwamnati na magance wannan rikicin ba zai taba faruwa a karkashin gwamnatin PDP ko gwamnatin da zan sa ido a kai ba.

“Na kasance ina saka hannun jari a fannin ilimi tun shekaru 30 da suka gabata.”

Tsohon mataimakin shugaban kasar ya yi alkawarin hada hannu da hukumomin jami’ar wajen ganin an kawo karshen yajin aikin da ake fama da shi.

“Na yi imanin PDP ta samar muku da mafi kyawun tsarin da za ku iya aiwatar da burin ku na gama gari,” in ji shi.

ASUU ta shiga yajin aikin ne tun ranar 14 ga watan Fabrairu saboda gazawar gwamnatin tarayya wajen mutunta yarjejeniyar da suka kulla a shekarar 2009.

latest nigeria newstoday

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp