fidelitybank

Ba zan sauka ba duk da kiran da a ke yi min – Shugaban PDP

Date:

Shugaban jam’iyyar PDP a Najeriya Iyorchia Ayu ya ce ko a jikinsa game da kiraye-kirayen da wasu suke yi cewa ya sauka daga kan mukaminsa.

Kazalika ya ce, masu yin hakan yara ne da ba su fahimci manufofin kafa jam’iyyar ba.

A hirarsa da BBC, tsohon dan Majalisar Dattawan ya ce, a iya saninsa ‘yan kasar ne suka zabe shi bisa sharuddan da jam’iyyarsu ta shata.

Ya kara da cewa, ko a lokacin da za su gudanar da zaben shugabannin PDP na kasa, an yanke cewar ba za a yi la’akari da bangaren da shugaban jam’iyyar ya fito ba wurin fid da dan takarar shugaban kasar.

An jima ana kai ruwa rana tsakanin jam’iyyar da dan takarar shugaban kasa da ya sha kaye a zaben fid da gwani, wato gwamnan Rivers Nyesom Wike, wanda rahotanni suka ce ya gindaya sharuddan ci gaba da zama jam’iyyar, da kuma mara wa Atiku Abubakar baya a matsayin dan takararta a zaben 2023.

Daga cikin sharuddan akwai bukatar Shugaban jam’iyyar Iyorchia Ayu, wanda ya fito daga Arewacin Najeriya ya sauka daga mukaminsa.

Sai dai a martanin da ya yi da BBC ta tambaye shi, Mr Ayu ya ce ba bu inda za shi, la’akari da cewa an zabe shi ne bisa dokokin da jam’iyyar PDP ta shimfida, a don haka ba zai sauka ba saboda kawai wasu ba sa son ganin shi a kai.

legit.ng.news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp