fidelitybank

Ba zan sake zama shugaban ƙasa ba a Najeriya – Goodluck

Date:

Yayin da ake ta kiranye ya dawo kan mulki, tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan, ya bayyana dalilin da ya sa ba zai sake tsayawa takarar shugabancin kasa ba.

Jonathan ya ce, ba zai iya sake tsayawa takarar Shugaban kasa ba saboda an kore shi a zaben 2015.

Tsohon Shugaban kasar ya ce, zai rage wa kansa ne ta hanyar zabar fom ya fara jan hankalin mutane da sake yakin neman zabe.

Ya bayyana hakan ne a cikin wani littafi mai suna ‘My Time As Chaplain in Aso Rock’ wanda Nathaniel Bivan ya rubuta, wanda ya yi cikakken bayani kan tarihin Chaplain na Aso Rock Villa Chapel a zamanin Jonathan, Obioma Onwuzurumba.

An gabatar da littafin ga jama’a a ranar Talata.

Sai dai da yake tsokaci a kan kungiyar da ta sayi fom din takarar shugaban kasa na jam’iyyar All Progressives Congress, APC a kan Naira miliyan 100, Jonathan ya ce, ya ji dadi domin ba zai sake zama shugaban kasa ba.

Wata kungiya da makiyaya da almajirai sun saya wa Jonathan fom din tsayawa takara a APC Naira miliyan 100 gabanin zaben fidda gwani na jam’iyyar.

Jonathan ya ce, “Na ji dadin sosai. Ko kadan basa zagina. Bayan haka, an kore ni daga ofishin cewa ban isa ba. Don haka, idan yanzu ’yan Najeriya suna cewa, ‘Oh, mutumin nan ya zo,’ wato suna share ni. Don haka.

“Idan kun tashi gobe kuma ku ga cewa ni ne Shugaban kasa kuma, hakan yana nufin akwai yiwuwar an sami wasu yanayi da suka fi karfina. Amma ba wai a je a dauko fom daya a je a fara rarrashin jama’a da yin yakin neman zabe ba, ko mulki na PDP ne ko tsintsiya madaurinki daya da APC ta zarce a fadin Najeriya. Ba zan iya sake yin hakan ba; idan na yi haka, zan rage kaina.”

tribune

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp