fidelitybank

Ba zan sake tsayawa takara ba idan na faɗi zaɓe – Trump

Date:

Tsohon shugaban ƙasar Amurka kuma ɗan takara a zaɓen nan mai tafe Donald Trump ya ce matuƙar ya faɗi zaɓe a wannan karon, to ba zai sake tsayawa takara ba.

Wannan ne karo na uku da Trump mai shekara 78 yake yi wa jam’iyyar Republican takara a jere.

A wata tattaunawa da ya yi da rukunin kafofin sadarwa na Sinclair, da aka tambaye shi ko yana tunanin sake yin takara idan Kamala Haris ta doke shi, sai ya ce, “Ba na tunanin haka,” in ji shi.

Sai dai ya ƙara da cewa yana da “ƙarfin gwiwar” samun nasara a zaɓen.

Dokokin a Amurka sun ƙayyade zango biyu ne ga shugaban ƙasa, wanda hakan ke nufin Trump ba zai iya zarce shekarar 2028 ba idan ya samu nasara.

A baya ba a cika jin Trump yana batun yiwuwar faɗuwa zaɓe ba, amma a cikin kwana huɗu da suka gabata, wannan ne karo na biyu da yake bayyana irin wannan maganar.

A wani taro da cibiyar Isra’ila da Amurka ta shirya a ranar Alhamis, ya yi maganar yiwuwar faɗuwar zaɓe, inda ya ce idan ya faɗi, hakan ba zai rasa nasaba da rashin goyon bayan Yahudawa ba.

Ya ce, “Sun san abin da zai faru idan ban ci zaɓen nan ba kuwa?” in ji shi kamar yadda kafofin watsa labarai da dama suka ruwaito.

“Ya kamata Yahudawa su yi wani abu saboda idan yanzu aka ce ina da goyon baya kashi 40 ne, hakan na nufin kashi 60 na wajen maƙiya ne.”

Sai dai kwamitin yaƙin zaɓen Kamala sun yi watsi da jawabin na Trump.

bbc news nigeria today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp