Shugaban Nkasa, Bola Tinubu ya ce, ko alama gwamnatinsa ba za ta lamunta da duk wani abu da zai raba kan al’ummar kasar ba.
Shugaban ya bayyana haka ne lokacin da ya karbi bakuncin jakadiyar kasar Finland a Najeriya, Sanna Selin, a fadarsa da ke Abuja a jiya Juma’a.
A lokacin ganawar tasu Tinubu ya bayyana farin cikinsa kan yadda hukumomin Finland suka tsare Simon Ekpa, jagoron wani bangare na haramtacciyar kungiyar masu fafutukar kafa kasar Biafra (Ipob), wanda ke zaune a can.
Hukumomin Finland sun kama Ekpa wanda dan Najeriya ne da ke da takardar zama dan kasar ta Turai sakamakon abubuwan da yake yi daga can da ke janyo ce-ce-ku-ce tare da haddasa tashin hankali a yankin kudu maso gabashin Najeriya.
Wannan shi ne karon farko da shugaban na Najeriya ya yi magana a kan Ekpa, tun bayan kama dantawayen a shekarar da ta wuce a kan zarin ta’addanci.
A nata bangaren jakadiyar Finland din ta bayyana cewa Simon Ekpa na haifar da cikas a dangantaka tsakanin kasashen biyu.
Kuma a yanzu bayan tsare shi alaka ta ci gaba da wanzuwa da kyau tsakanin kasashen.
Hukumomin Finland sun kama Ekpa wanda dan Najeriya ne da ke da takardar zama dan kasar ta Turai sakamakon abubuwan da yake yi daga can da ke janyo ce-ce-ku-ce tare da haddasa tashin hankali a yankin kudu maso gabashin Najeriya.
Wannan shi ne karon farko da shugaban na Najeriya ya yi magana a kan Ekpa, tun bayan kama dantawayen a shekarar da ta wuce a kan zarin ta’addanci.
A nata bangaren jakadiyar Finland din ta bayyana cewa Simon Ekpa na haifar da cikas a dangantaka tsakanin kasashen biyu.
Kuma a yanzu bayan tsare shi alaka ta ci gaba da wanzuwa da kyau tsakanin kasashen.