fidelitybank

Ba zan gudu ba daga Najeriya saboda EFCC – Wike

Date:

Gwamna Nyesom Wike na jihar Ribas, ya ce, ba zai gudu daga Najeriya ba, saboda tsoron hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa, EFCC, bayan ranar 29 ga watan Mayu da wa’adinsa ya kare.

Wike ya ce, zai yi farin ciki da karrama EFCC idan aka gayyace shi a karshen wa’adinsa a ranar 29 ga watan Mayu.

Gwamnan ya mayar da martani ne kan fallasa kwanan nan da Shugaban Hukumar EFCC, Abdulrasheed Bawa ya yi na cewa, hukumar za ta kama wasu gurbatattun gwamnonin da wa’adinsu ya kare a ranar 29 ga watan Mayu.

Karanta Wannan: Ina goyon bayan dakatar da Ayu daga PDP – Wike

Sai dai Wike ya ce, bai damu da barazanar kama gwamnonin ba a karshen wa’adinsu a ranar 29 ga Mayu.

Gwamnan yayi magana a shirin karin kumallo na Channels Television, SUNRISE a ranar Litinin.

Wike ya sha alwashin ba zai gudu daga Najeriya kwanaki kafin rantsar da wanda zai gaje shi kamar yadda wasu tsofaffin gwamnoni suka yi a baya.

“Ba zan gudu ba saboda EFCC. Me yasa zasu gayyace ni? Idan sun gayyace ni, zan girmama gayyatarsu. Ba zan gudu ba,” in ji Wike.

vgn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp