fidelitybank

Ba zan daina sukar Buhari ba har sai an daina kashe al’umma – Ortom

Date:

Gwamnan jihar Binuwai, Samuel Ortom, ya ce, ba shi da wani abu na kashin kansa ga shugaban kasa Muhammadu Buhari.

Ya bayyana cewa yana sukar shugaban kasa ne kawai kan rashin iya kawo karshen kashe-kashen da ake yi a jihar da kuma Najeriya.

Gwamnan ya mayar da martani ne ga wata sanarwa da Shugaban Ilimin Manyan Makarantu na Majalisar Wakilai, Aminu Suleiman Goro ya yaba wa Shugaban Kasa Muhammadu Buhari a lokacin kaddamar da wasu ayyuka a Jami’ar Aikin Gona ta Tarayya da ke Makurdi.

An ruwaito cewa shugaba Buhari ya roki gwamna Ortom da ya yi kokarin amincewa da manyan ayyukan gwamnatinsa a jihar Benuwe maimakon yi masa zagon kasa.

Amma Gwamnan a jawabinsa a ranar Asabar, 1 ga Oktoba, 2022 a hidimar bikin Independence Day a Interdenominational Church wanda gwamnatin jihar ta shirya tare da kungiyar Kiristoci ta Najeriya, CAN, ya jaddada cewa, ba shi da wani abu na kashin kansa a kan shugaban kasa face ya damu da kashe-kashen da ake yi wa al’ummarsa.

Taron ya gudana ne a cocin Faith Cathedral of All Nations Evangelism Ministry, Old GRA, Makurdi.

Gwamnan ya tambayi dalilin da ya sa ya daina sukar Shugaban kasa a kullum ana kashe al’ummar Binuwai, ba tare da gwamnatin tarayya ta iya kawo karshen hakan ba, yana mai jaddada cewa, “Ba zan daina suka ba har sai an daina kashe-kashen,” Gwamnan ya bayyana.

naija hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Jihohi 19 da za a yi kwana 9 a na ruwan sama harda Kano – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta yi hasashen za a shafe kwana...

Tinubu ya mika sakon ta’aziyya bisa rasuwar matar MKO Abiola

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya miƙa saƙon ta'aziyyarsa bisa...

Abubuwan da Kwamiti ya gano a wajen Kwamishina mai murabus na Kano

A ranar Litinin ne kwamitin binciken badaƙalar belin Danwawu,...

Bajintar ɗaliban Najeriya a gasar Turanci ta nuna ingancin ilimi a ƙasa – Tinubu

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu, ya taya ƴanmatan nan uku...

Ƙudirin faɗaɗa mamayar Gaza zai ƙara jefa Falasɗinawa cikin hatsari – MDD

Majalisar Ɗinkin Duniya ta bayyana rahotannin da ke kwarmata...

APC a Kano mu na jinjinawa Tinubu – Abdullahi Abbas

Shugabannin jam’iyyar APC a jihar Kano, sun yabawa shugaba...

Kwamishinan da ake tuhuma da belin dilan kwayoyi a Kano ya yi murabus

Kwamishinan Sufuri na Jihar Kano, Ibrahim Ali Namadi ya...

Turji ya saki Mutane 32 bayan zaman sulhu

Shahararren shugaban ‘yan bindiga, Bello Turji, ya saki mutane...

ADC ta gargadi El’Rufa’i kan ruguza jam’iyyar

Shugaban jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) a jihar Kaduna,...

An gindayawa Thomas Partey sharudan beli

An gindaya sharuddan belin tsohon dan wasan tsakiya na...

Fursunoni 37 na jiran zartas musu da hukuncin kisa a Bauchi

Fursunoni 37 da aka yanke wa hukuncin kisa bisa...

Kwamitin sulhu na MDD zai gana kan makomar ƴan Isra’ila da ke hannun Hamas

Kwamitin tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya zai tattauna yau...
X whatsapp