Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari, ya yi kira ga ‘yan Najeriya da su guji mutanen da ke ƙoƙarin ganin sun karya doka a faɗin kasar.
Wata sanarwa da kakakin shugaban kasar, Malam Garba Shehu, ya aike wa manema labarai ta rawaito cewa, Buhari ya na mai tabbatar wa ‘yan kasa cewa, ba zai kyale wani ya karya dokokin kasar ba.
”Muna da kasa, muna da albarkatun kasa da kuma mutane. Sai dai ban san dalilin da ya sa wasu ke da niyyar ba da kansu ba, wajen lalata ƙasarsu ba,” a cewar Buhari yayin buɗe baki da ya yi da gwamnoni da ministoci a Abuja ranar Talata.
Shugaban ya sake jaddada cewa, ƙaddamar da amfani da fasahar na’urar tantance masu kaɗa ƙuri’a ba za ta bari wani ya yi iƙirarin samun miliyoyin ƙuri’u yayin babban zaɓe na 2023 mai zuwa.