Kocin Manchester City, Pep Guardiola, ya ce ba shi ne mutumin da ya dace ya ba Ruben Amorim shawara ba.
A ranar Juma’a ne aka tabbatar da Amorim a matsayin kocin Manchester United na gaba.
Dan wasan mai shekaru 39, zai maye gurbin Erik Ten Hag, wanda aka kora ranar Litinin, bayan da West Ham ta sha kashi da ci 2-1.
An tambayi Guardiola game da labarin, musamman yayin da zai fuskanci Amorim ‘Sporting Lisbon a gasar zakarun Turai mako mai zuwa.
Ya amsa: “Ba ni ne mutumin da ya dace in ba abokan aikina shawara ba.
“United na da mutane da yawa da za su gaya masa halin da ake ciki a kulob din. Ba zan iya ba shi wata shawara ba.”