Sabuwar babbar mai shari’a ta kasa, Mai shari’a Kudirat Kekere-Ekun ta ce ko kaɗan ba za ta lamunci cin hanci da rashawa ba a ɓangaren shari’ar Najeriya a ƙarƙashin mulkinta.
“Dukkan wasu matsalolin da suka shafi kafin zaɓe dole a kammala su a Kotun Ɗaukaka Ƙara,” in ji ta, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.
Kudirat Kekere-Ekun ta bayyana hakan ne bayan Majalisar Dattawa ta tabbatar da ita a matsayin Babbar mai shari’a ta ƙasar ranar Laraba.
Shugaban ƙasar Najeriya Bola Tinubu ne dai ya aika da buƙatar hakan kasancewa ta riƙe muƙamin a matsayin muƙaddashiya tun watan Agusta bayan Mai shari’a Olukayode Ariwoola ya yi ritaya.
Mai shari’ar ta kuma bayyana cewa za ta yi amfani da fasahar zamani domin tabbatar da ganin ana gudanar da shari’a cikin sauri, sannan ta ƙuduri aniyar tabbatar da ƴancin ɓangaren shari’a.
Ita ce dai Babbar shari’a ta 23 a Najeriya, kuma mace ta biyu a matsayin.