Kungiyar Kiristoci ta kasa, ta yi alkawarin kin zabar jam’iyyar APC mai mulki a zaben shugaban kasar da ke tafe a shekara mai zuwa, bayan da dan takarar shugaban kasar karkashin jam’iyyar Bola Ahmed Tinubu ya zabi sanata Kashim Shetima a matsayin mataimakinsa.
Shi dai Tinubu da Khashim Shettima duka musulmai ne abinda da kungiyar ke kallon tamkar mayar da addininsu saniyar ware da jam’iyyar ta yi.
Jaridar Punch ya rawaito cewa, kungiyar na cewa wannan mataki da jam’iyyar ta dauka babban kuskure ne a siyasance a kasa irin Najeriya da ke da akidar bangaranci a siyasarta.
Kungiyar kiristoci ta mabiya Pentecostal (PFN) na cewa za su shawarci mabiyansu da kada su zabi jam’iyyar ta APC.
Tuni dai Tinubun ya kare matakin nasa, yana mai cewa ya fifita cancanta ne fiye da addini a zabin nasa.
Kiristoci da kungiyoyin fararen hula a kasar dai sun sha yi wa dan takarar gargadin daukar musulmi a matsayin mataimaki a zaben na watan Febrairu mai zuwa.
Tuni dai dan takarar babbar jam’iyyar adawa ta PDP Atiku Abubakar wanda musulmi ne, ya zabi gwamnan jihar Delta Ifeanyi Okowa, wanda kirista ne a matsayin mataimakinsa.