Shugaban Rwanda ya ce, ba za su yarda wata kasa ta ci gaba da tankwara su ba kan harkokin da suka shafi cikin gidansu ba.
Shugaban na Rwanda na bayyana hakan ne a matsayin martani ga bukatar da gwamnatin Amurka ta gabatar masa ta sakin wani mai kalubalantar gwamnatin kasar Paul Rusesabagina.
A yayin tattanauwa kan matsalolin da suka shafi Afirka a taron shugaban kasashen nahiyar da aka gudanar a Washington, an tambayi Kagame ko bukatar da wakilin Amurka Antony Bilinken ya gabatar ta sako shari’ar da ake yi wa Mr Rusesabagina, na “taimako ko bata masa rai”.
Mr Kagame ya ce, wani da ke Amurka na so a yi bar shari’ar, saboda mutumin tauraro ne.”
A shekarar da ya gabata ne aka sami wasu Rusesabagina da wasu mutanen da laifin ayyukan ta’addanci.
Mr Kagame ya ce “idan muka sake shi, su kuma sauran mutum 20 din da suka nuna shi a matsayin shugaban su.”
Mr Rusesabagina, mai shekaru 68, ya kasance jarumi na finafinan Hollywood, kan filin din kisan kiyashin da aka yi a Rwanda.
An yanke masa hukucin daurin shekaru 25 a gidan yari bayan da aka yaudare shi hawa jirigin daga dubai zuwa birnin Riwanda Kigali, a tunanin zai wuce zuwa Burundi. Inji BBC.