Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), ta yi watsi da bukatar da jam’iyyun siyasa suka yi na a daidaita jadawalin zaben 2023, na baiwa jam’iyyu karin lokaci, domin shiryawa da gudanar da zabukan fidda gwani.
Jam’iyyun siyasa a kasar sun bukaci hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) da ta kara wa’adin gudanar da zabukan shekarar 2023 da watanni biyu.
Musamman, jam’iyyun na son ’yan sauye-sauye ga jadawalin zaben fidda gwani, kamar yadda alkalan zaben suka gindaya.
Shugaban kungiyar masu ba da shawara ta jam’iyyu (IPAC) Yusuf Yabagi ne ya yi wannan roko a ranar Talata, a wani taron alkalan zabe da shugabannin jam’iyyun siyasa daban-daban a hedikwatar INEC da ke Abuja.