Shugaban Ukraine Volodymyr Zelensky ya ce ƙasarsa na ci gaba da fafatawa a yankin Donbas kuma “ba ta da niyyar saranda”.
Cikin wata hira da ya yi da kafar talabijin ta CNN, Zelensky ya yi watsi da batun sakar wa Rasha yankin Donbas da wasu yankunan gabashin ƙasar a matsayin sharaɗin kawo ƙarshen yaƙin.
Ya ƙara da cewa: “Ukraine da mutanenta sun faɗa ƙarara. Ba mu mamaye ƙasar kowa ba kuma mu ma ba za a mamaye tamu ba.”
Duk lokacin da Shugaban Rasha Putin ya yi magana kan ƙwace yankin Donbas, yana magana ne kan tsohon garin da ake samar da ƙarafa da gawayin kwal na Ukraine.
Abin da yake nufi takamaimai shi ne ɗaukacin yankin gabashi mai girma na Luhansk da Donetsk wanda ya fara tun daga ƙarshen Mariupol daga kudu har zuwa kan iyaka daga arewaci.