Ministan ma’adinai da karafa, Olamilekan Adegbite, ya ce, ba za a kammala gyaran kamfanin karafa na Ajaokuta ba kafin karshen wa’adin shugaban kasa Muhammadu Buhari a ranar 29 ga Mayu, 2023.
Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da yakin da ya hada da Rasha da Ukraine ya janyo asarar dala biliyan biyu na yarjejeniyar gyaran karafa ta Ajaokuta da ke jihar Kogi.
A cewar Ministan, “A watan Oktoba na 2019, Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari da Vladmir Putin na Rasha sun gana a taron Rasha da Afirka a Sochi inda suka amince da farfado da kamfanin sarrafa karafa na Ajaokuta.”
Ya lura da cewa, matsalolin da ke haifar da barkewar cutar ta COVID-19 a duniya kuma sun jinkirta fara aikin.
Adegbite, bai bayyana sunan kamfanin na Burtaniya da zai gudanar da aikin ba a nan gaba