Gwamnatin tarayya ta tabbatar da cewa, ba za ta iya kwashe ƴan Najeriya ba a Ukraine, har sai an buɗe filayen jiragen sama a ƙasar da ke fuskantar hare-haren Rasha.
Rasha na ci gaba da kai hare-hare a Ukraine, bayan da shugaba Putin ya bayar da umarnin mamaye ƙasar.
Ma’aikatar harakokin wajen Najeriya ta ce, ƴan Najeriya 5,600 ne a Ukraine, kuma yawancinsu ɗalibai ne.
Ƙungiyar ɗaliban ta yi kira ga shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari da ya gaggauta kwashe su daga Ukraine.
A ranar Juma’a ministan harakokin wajen Najeriya Geoffrey Onyeama, ya ce, gwamnati ta damu da halin da ƴan Najeriya ke ciki a Ukraine. In ji BBC.