fidelitybank

Ba zamu fitar da jadawallin zabe ba sai mun ga abun da ya biyo ba – INEC

Date:

Shugaban hukumar zaɓe mai zaman kanta ta INEC, Farfesa Mahmud Yakubu, ya ce, hukumar na ci gaba da jiran ganin abin da zai biyo baya a ƙudirin gyaran dokar zaɓe da ke gaban shugaban ƙasa kafin su faɗi jadawalin babban zaɓen 2023.

Yayin ganawa da manema labarai, Farfesa Mahmud, ya ƙara da cewa, shugaban majalisar dattawa, Ahmad Lawan ya ba su tabbacin cewa ‘yan majalisar za su mayar da hankali kan gyaran dokar da zarar sun koma bakin aiki a yau Talata daga hutun ƙarshen shekara da suka yi.

“Muna jiran saka wa ƙudirin dokar zaɓe hannu cikin sauri, wadda take da matuƙar muhimmanci ga harkokin zaɓen mu. Da zarar ta zama doka, nan take za mu fitar da jadawalin ayyuka na babban zaɓen 2023 bisa tsarin sabuwar dokar, “ a cewar Farfesa Yakubu.

Shugaba Buhari ya bayyana cewa, ya ƙi amincewa ya saka wa dokar hannu, saboda ‘yan majalisa sun haƙiƙance cewa, wajibi ne jam’iyyu su fitar da ‘yan takara ta hanyar zaɓen yar tinƙe, ya na mai cewa “Dole ne a bai wa mutane zaɓi”.

Kafin su tafi hutun, ‘yan majalisar sun sha alwashin yin amfani da damar da Kundin Tsarin Mulki ya ba su wajen tsallake shugaban ƙasa kuma su saka wa dokar hannu.

www.legitnews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...
X whatsapp