Shugaban hukumar zaɓe mai zaman kanta ta INEC, Farfesa Mahmud Yakubu, ya ce, hukumar na ci gaba da jiran ganin abin da zai biyo baya a ƙudirin gyaran dokar zaɓe da ke gaban shugaban ƙasa kafin su faɗi jadawalin babban zaɓen 2023.
Yayin ganawa da manema labarai, Farfesa Mahmud, ya ƙara da cewa, shugaban majalisar dattawa, Ahmad Lawan ya ba su tabbacin cewa ‘yan majalisar za su mayar da hankali kan gyaran dokar da zarar sun koma bakin aiki a yau Talata daga hutun ƙarshen shekara da suka yi.
“Muna jiran saka wa ƙudirin dokar zaɓe hannu cikin sauri, wadda take da matuƙar muhimmanci ga harkokin zaɓen mu. Da zarar ta zama doka, nan take za mu fitar da jadawalin ayyuka na babban zaɓen 2023 bisa tsarin sabuwar dokar, “ a cewar Farfesa Yakubu.
Shugaba Buhari ya bayyana cewa, ya ƙi amincewa ya saka wa dokar hannu, saboda ‘yan majalisa sun haƙiƙance cewa, wajibi ne jam’iyyu su fitar da ‘yan takara ta hanyar zaɓen yar tinƙe, ya na mai cewa “Dole ne a bai wa mutane zaɓi”.
Kafin su tafi hutun, ‘yan majalisar sun sha alwashin yin amfani da damar da Kundin Tsarin Mulki ya ba su wajen tsallake shugaban ƙasa kuma su saka wa dokar hannu.