fidelitybank

Ba zamu fitar da jadawallin zabe ba sai mun ga abun da ya biyo ba – INEC

Date:

Shugaban hukumar zaɓe mai zaman kanta ta INEC, Farfesa Mahmud Yakubu, ya ce, hukumar na ci gaba da jiran ganin abin da zai biyo baya a ƙudirin gyaran dokar zaɓe da ke gaban shugaban ƙasa kafin su faɗi jadawalin babban zaɓen 2023.

Yayin ganawa da manema labarai, Farfesa Mahmud, ya ƙara da cewa, shugaban majalisar dattawa, Ahmad Lawan ya ba su tabbacin cewa ‘yan majalisar za su mayar da hankali kan gyaran dokar da zarar sun koma bakin aiki a yau Talata daga hutun ƙarshen shekara da suka yi.

“Muna jiran saka wa ƙudirin dokar zaɓe hannu cikin sauri, wadda take da matuƙar muhimmanci ga harkokin zaɓen mu. Da zarar ta zama doka, nan take za mu fitar da jadawalin ayyuka na babban zaɓen 2023 bisa tsarin sabuwar dokar, “ a cewar Farfesa Yakubu.

Shugaba Buhari ya bayyana cewa, ya ƙi amincewa ya saka wa dokar hannu, saboda ‘yan majalisa sun haƙiƙance cewa, wajibi ne jam’iyyu su fitar da ‘yan takara ta hanyar zaɓen yar tinƙe, ya na mai cewa “Dole ne a bai wa mutane zaɓi”.

Kafin su tafi hutun, ‘yan majalisar sun sha alwashin yin amfani da damar da Kundin Tsarin Mulki ya ba su wajen tsallake shugaban ƙasa kuma su saka wa dokar hannu.

naija news legit

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sanatocin Arewa sun yi tir da kisan Zamfara

Ƙungiyar sanatocin Arewa, ta yi Allah wadai da kisan...

Tattalin arzikin Najeriya zai kara bunkasa a shekarar nan – IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta...

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuɗa

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiɗa wa Isra'ila wasu...

‘Yan Arewa su dakata da neman mulki har zuwa 2031 – Sakataren Gwamnati

Sakataren gwamnatin tarayya, SGF, George Akume, ya yi kira...

Matatar Dangote ta janye ƙarar da ta shigar kamfanin NNPCL a kotu

Matatar man Dangote ta janye ƙarar da ta shigar...

Ba mu baiwa Obi shawara ya janye daga takara ba – Kungiyar Inyamurai

Kungiyar koli ta al’adun kabilar Igbo, Ohanaeze Ndigbo Worldwide,...

Dole ne APC ta bar mana kujerar mataimakin shugaban kasa – ANPP

Tsagin tsohuwar jam'iyyar All Nigeria Peoples Party wato ANPP...

Gwamna ya nada Sarkin Gusau

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal ya amince da naɗin...

‘Yan Bindiga sun yi ikirarin kashe Daliban koyon aikin lauya a Benuwai

Ƴanbindiga da suka yi garkuwa da ɗaliban makarantar samun...

Tinubu ya gwangwaje tawagar Super Falcons da ruwan daloli da gidaje a Abuja

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bai wa ƴan wasan...
X whatsapp