Jami’an Rasha sun zargi kafar YouTube da toshe shafin majalisar wakilan ƙasar.
Rasha ta ce, Amurka ta keta haƙƙin da ƴan Rasha suke da shi, kamar yadda Vyacheslav Volodin, shugaban majalisar ta Duma ya bayyana.
“Amurka na son mallake dukkanin bayanai, in ji Volodin a Telegram yana mai cewa “ba za mu amince ba.”