Tsohon kyaftin din kungiyar Super Eagles, Joseph Yobo da wasu shugabannin matasa sun kaddamar da wani shiri mai suna Grassroots Mobilisation Initiative a ranar Litinin a Abuja.
A cewarsu, GMI an tsara shi ne domin samar da wata kafa ta zaburar da goyon bayan matasan Najeriya, wajen gudanar da ayyuka masu tarin yawa wanda zai tabbatar da cewa, masu sahihanci ne kawai za su karbi mulki a 2023, musamman a fadar shugaban kasa.
Yobo, a jawabin da ya gabatar a wajen taron, ya bayyana bakin cikinsa kan gazawar shugabanni wajen tunkarar kalubalen rashin tsaro, da tabarbarewar tattalin arziki, da cin hanci da rashawa, da talauci da ba a taba ganin irinsa ba.
Ya ce, “Mun yarda cewa Najeriya aiki ne da ke kan gaba. A matsayinmu na al’umma, mun dan samu ci gaba, amma muna son kari, a hakikanin gaskiya, da yawa. Idan ka dubi kasar a halin yanzu, ba mu kasance inda ya kamata mu kasance ba.
“A baya-bayan nan ne ni da wasu masu irin wannan tunani muka dauki kanmu mu hadu mu yi magana domin amfanin kasarmu. Muna son sabon shugaba wanda zai karfafa kyawawan nasarorin da ake samu da kuma ciyar da Najeriya gaba.
“Zaben 2023 na da matukar muhimmanci ga makomar kasarmu. Daga Arewa zuwa Kudu, daga Gabas zuwa Yamma, dole ne a sa baki da yan Nijeriya.