Shugaban jam’iyyar APC na kasa, Abdullahi Adamu, ya bukaci ‘ya’yan jam’iyyar da su yi aiki tare da juna, domin tabbatar da nasara a zaben 2023 mai zuwa.
Malam Adamu ya yi wannan kiran ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai.
Ya yi gargadin cewa, ba zai amince da laifin faduwar zabe ba.
“Dole ne mu yi wasu ayyuka mu manta da wasu na son zuciya mu tsaya tare. Ba ma son wani ya zo nan bayan zabe ya fara kuka yana dora mana laifin gazawarmu. Ba zan saurari hakan ba. Wannan shi ne lokacin da za a haɗa kai. Wannan shine lokacin yin aiki don haɗin kai. Idan muka yi haka, Allah zai kasance tare da mu,” inji shugaban jam’iyyar APC.
Ya ce, an gudanar da gagarumin taro tsakanin shugabannin jam’iyyar a Abia kafin kaddamar da kwamitin.
Adamu ya kara da cewa, sun shiga tattaunawa da kwamitin gudanarwa na kasa (NWC), musamman a lokacin zaben fidda gwani da kuma bayansa, inda ya bayyana kwarin guiwar kwamitin zai tabbatar da zaman lafiya a yankin Abia na jam’iyyar APC.


