Tsohon shugaban majalisar dattawa, Bukola Saraki ya kalubalanci shirin gwamnatin tarayya na kashe kudaden tallafin man fetur bisa dogaro da lita miliyan 70 da ake amfani da shi a rana.
Tsohon shugaban majalisar dattawan, Bukola Saraki, ya bayyana hakan ne a wata hira da gidan talabijin na Channels TV a yammacin Lahadi.
Bukola ya ce, man fetur din Najeriya ba zai iya wuce lita miliyan 35 a rana ba, ya kuma yi nuni da cewa, Najeriya na iya bayar da tallafin man fetur, makwabciyarta kasashen Yammacin Afrika.
Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya mikawa majalisar dokokin daftarin kasafin kudin shekarar 2022 wanda ya gyara a watan da ya gabata, inda gwamnatin tarayya ta ware Naira tiriliyan 2.557, domin tallafin man fetur sakamakon dakatar da aiwatar da manufofin da gwamnatin tarayya ta yi.