Kungiyar Dattawan Arewa (NEF) ta bayyana dalilin da ya sa ba ta amince da duk wani dan takarar shugaban kasa da za a yi a ranar 25 ga watan Fabrairu.
Hakeem Baba-Ahmed, mai magana da yawun kungiyar ta NEF, ya ce kungiyar ba za ta yi gaggawar amincewa da duk wani dan takarar shugaban kasa ba, duk da cewa zabe na karatowa.
Kamar yadda Premium Times ta ruwaito, Baba-Ahmed ya bayyana hakan ne a lokacin da ya fito a matsayin bako a wani shiri kai tsaye da gidan Talabijin mai zaman kansa na Afrika (AIT).
Baba-Ahmed ya ce, NEF na tantance manyan ‘yan takara ta fuskar abin da suke yi da kuma fadin su.
Ya ce kungiyar ta arewa tana kuma tantance ‘yan takarar wasu kujeru da suka hada da ‘yan majalisar tarayya da na gwamnoni. “Mun yi imanin cewa mulki ba wai mutum daya ne kawai ba, shi ya sa ba mu yi gaggawar cewa wannan shi ne dan takararmu ba saboda mutum daya ba zai iya canza kasar nan ba,” inji shi.
Ya ce ‘yan Najeriya na bukatar “shugaban kasa mai jajircewa” da zai dauki matakin da ba zai yi farin jini a tsakanin jama’a ba. A cewar Baba-Ahmed, kasa mafi yawan al’umma a Afirka ba ta bukatar shugaban kabila ko kuma wanda aka zabe shi bisa addini.