fidelitybank

Ba za mu yi gaggawar amincewa da ‘yan takara ba – Kungiyar Dattawan Arewa

Date:

Kungiyar Dattawan Arewa (NEF) ta bayyana dalilin da ya sa ba ta amince da duk wani dan takarar shugaban kasa da za a yi a ranar 25 ga watan Fabrairu.

Hakeem Baba-Ahmed, mai magana da yawun kungiyar ta NEF, ya ce kungiyar ba za ta yi gaggawar amincewa da duk wani dan takarar shugaban kasa ba, duk da cewa zabe na karatowa.

Kamar yadda Premium Times ta ruwaito, Baba-Ahmed ya bayyana hakan ne a lokacin da ya fito a matsayin bako a wani shiri kai tsaye da gidan Talabijin mai zaman kansa na Afrika (AIT).

Baba-Ahmed ya ce, NEF na tantance manyan ‘yan takara ta fuskar abin da suke yi da kuma fadin su.

Ya ce kungiyar ta arewa tana kuma tantance ‘yan takarar wasu kujeru da suka hada da ‘yan majalisar tarayya da na gwamnoni. “Mun yi imanin cewa mulki ba wai mutum daya ne kawai ba, shi ya sa ba mu yi gaggawar cewa wannan shi ne dan takararmu ba saboda mutum daya ba zai iya canza kasar nan ba,” inji shi.

Ya ce ‘yan Najeriya na bukatar “shugaban kasa mai jajircewa” da zai dauki matakin da ba zai yi farin jini a tsakanin jama’a ba. A cewar Baba-Ahmed, kasa mafi yawan al’umma a Afirka ba ta bukatar shugaban kabila ko kuma wanda aka zabe shi bisa addini.

legit com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An gargadi al’umma su yi taka tsan-tsan da ambaliyar ruwan sama

Yayin da ake ci gaba da fuskantar saukar ruwan...

Gwamnatin Tarayya za ta gina hanyar sufurin jirgin ƙasa a Kano

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta samar da titin...

Abin da ya sa muke ci gaba da tsare Sowore – Ƴansanda

Kwamishinan ƴansanda mai kula da sashen kai ɗauki na...

INEC za ta bai wa ɗaurarru damar kaɗa ƙuri’a a lokacin zaɓuka

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta ta duba yiwuwar bai...

Mai ya jawo Matan Zamfara su ka yi zanga-zanga

Ɗaruruwan mata ne tsofaffi da masu shawarya suka gudanar...

Aƙalla mutane 24,000 ne suka ɓata saboda Boko Haram a Najeriya

Kungiyar Agaji ta Red Cross ta bayyana cewa aƙalla...

‘Yansanda ku gaggauta sakin Sowore – Obi

Tsohon ɗan takarar shugaban kasa a jam'iyyar LP, Peter...

PDP ta gargaɗi mambobinta kan goyon bayan Tinubu

Babbar jam'iyyar hamayya ta PDP a Najeriya ta gargaɗi...

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman...

An fitar da jerin sunayen Matasan ‘yan wasan da za su lashe kyautar Kopa

Masu shirya kyautar Ballon d’Or, sun fitar da jerin...

An fitar da jerin masu tsaron raga da za su lashe kyautar gwarzon bana

An fitar da sunayen wadanda za a zaba don...

Jonathan ne ya fi cancanci ya rike Najeriya Farfesa Tukur

Farfesa Tukur Muhammad-Baba, Sakataren Yada Labarai na Kungiyar Tuntuba...
X whatsapp