fidelitybank

Ba za mu yarda mu mutu a cikin PDP ba shi yasa muka koma APC – Sanatoci

Date:

Sanatocin Najeriya uku da suka fito daga jihar Kebbi, waɗanda suka sauya sheƙa daga babbar jam’iyyar adawa ta PDP zuwa APC mai mulki sun ce, sun fita daga jam’iyyar ce sanadiyyar rikice-rikice na cikin gida.

A jiya Talata ne shugabancin majalisar dattajai ya tabbatar da sauya shekar sanatocin wato Sanata Adamu Aliero mai wakiltar Kebbi ta tsakiya da Yahaya Abdullahi mai wakilartar Kebbi arewa da kuma Garba Maidoki mai wakiltar Kebbi ta kudu.

Sanatocin sun ce sun fice daga jam’iyyar ne saboda rikice rikicen cikin gida da suka yi wa jam’iyyar PDP katutu.

Daya daga cikinsu, Sanata Yahaya Abdullahi ya shaida wa BBC cewa a bayyane take tun bayan zaɓen 2023, jam’iyyar PDP ta shiga ruɗani da rikici kala-kala, kuma har kawo yanzu babu alamun jam’iyyar tana ɗaukar matakin gyara matsalolin nata.

Ya ce ”Kowa ya san dai abubuwan da suka addabi PDP, tana son ta wargaje. Ba kuwa wanda ke son ya shigo mu’amula da jama’a sai ka ga waɗanda ka zo kana son ka zauna da su kana tsammanin za a haɗa kai a ceto al’umma a gyara ƙasa, sai kansu duk ya rarrabu, abu ya ƙi ci, ya ƙi cinyewa kullum sai ƙara lalacewa ya ke.”

Ya yi bayanin cewa ai dama can da su aka kafa APC amma sun fice daga cikin ta ne saboda gwamnan su na wancan lokacin ya nuna baya yi da su, kuma sai PDP ta janye su, amma a yanzu yanayin ya canza domin kuwa asalin ƴan PDP su gaza ɗinke ɓarakar su ta cikin gida kuma ga shi a ”shugaban ƙasa Tinubu ya san amfanin mu, kuma shi sabon gwamna Dr Nasiru Idris Kauran Gwandu ƙaninmu ne, ya bamu girma ya bamu mutumcin mu, don haka irin wannan a kan me za mu zauna muna jayayya da shi.”

Sanata Yahaya Abdullahi ya kuma musanta cewa akwai alƙawarin da shugaba Tinuu ya yi masu, wanda ya sa suka sauya sheka zuwa APC inda ya ce shi a yanzu babu abin da bai gani ba a rayuwa domin haka ya wuce a yi mashi alƙawari kafin sauya sheƙa.

besda

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp