fidelitybank

Ba za mu yarda mu mutu a cikin PDP ba shi yasa muka koma APC – Sanatoci

Date:

Sanatocin Najeriya uku da suka fito daga jihar Kebbi, waɗanda suka sauya sheƙa daga babbar jam’iyyar adawa ta PDP zuwa APC mai mulki sun ce, sun fita daga jam’iyyar ce sanadiyyar rikice-rikice na cikin gida.

A jiya Talata ne shugabancin majalisar dattajai ya tabbatar da sauya shekar sanatocin wato Sanata Adamu Aliero mai wakiltar Kebbi ta tsakiya da Yahaya Abdullahi mai wakilartar Kebbi arewa da kuma Garba Maidoki mai wakiltar Kebbi ta kudu.

Sanatocin sun ce sun fice daga jam’iyyar ne saboda rikice rikicen cikin gida da suka yi wa jam’iyyar PDP katutu.

Daya daga cikinsu, Sanata Yahaya Abdullahi ya shaida wa BBC cewa a bayyane take tun bayan zaɓen 2023, jam’iyyar PDP ta shiga ruɗani da rikici kala-kala, kuma har kawo yanzu babu alamun jam’iyyar tana ɗaukar matakin gyara matsalolin nata.

Ya ce ”Kowa ya san dai abubuwan da suka addabi PDP, tana son ta wargaje. Ba kuwa wanda ke son ya shigo mu’amula da jama’a sai ka ga waɗanda ka zo kana son ka zauna da su kana tsammanin za a haɗa kai a ceto al’umma a gyara ƙasa, sai kansu duk ya rarrabu, abu ya ƙi ci, ya ƙi cinyewa kullum sai ƙara lalacewa ya ke.”

Ya yi bayanin cewa ai dama can da su aka kafa APC amma sun fice daga cikin ta ne saboda gwamnan su na wancan lokacin ya nuna baya yi da su, kuma sai PDP ta janye su, amma a yanzu yanayin ya canza domin kuwa asalin ƴan PDP su gaza ɗinke ɓarakar su ta cikin gida kuma ga shi a ”shugaban ƙasa Tinubu ya san amfanin mu, kuma shi sabon gwamna Dr Nasiru Idris Kauran Gwandu ƙaninmu ne, ya bamu girma ya bamu mutumcin mu, don haka irin wannan a kan me za mu zauna muna jayayya da shi.”

Sanata Yahaya Abdullahi ya kuma musanta cewa akwai alƙawarin da shugaba Tinuu ya yi masu, wanda ya sa suka sauya sheka zuwa APC inda ya ce shi a yanzu babu abin da bai gani ba a rayuwa domin haka ya wuce a yi mashi alƙawari kafin sauya sheƙa.

www.leadership ng.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojojin hadin gwiwa sun hallaka ‘yan Boko Haram a tafkin Chadi

Rundunar hadin gwiwa mai yaƙi da Boko Haram a...

Na yi rashin aboki na gari kuma Najeriya ta rasa mutumin kirki – Tinubu

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, na ci gaba da alhinin...

Shettima ya jagoranci yi wa Buhari addu’o’i na musamman a Daura

An gudanar da addu'o'i na musamman don neman gafara...

Isra’ila ta kashe mana fararen hula – Syria

Shugaban Syria, Ahmed al-Sharaa ya zargi Isra'ila da kai...

Za mu koma fadar gwamnatin Katsina mu karbi gaisuwar Buhari – Radda

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umar Radda ya ce bayan...

Tinubu zai jagoranci yi wa Buhari addu’a

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, zai jagoranci taron addu'o'i na...

Muƙarraban Buhari sun ci amanar da ya ba su lokacin mulkinsa – Bagos

Wani tsohon ɗan majalisar wakilai, Dachung Bagos ya bayyana...

Guardiola ya bude kofa ga ‘yan wasa shida su bar kungiyar

Kocin Manchester City, Pep Guardiola, a shirye yake ya...

Ba gudu ba ja da baya a zanga-zangar mu – Tsofaffin ‘Yansanda

Kungiyar ‘yan sandan Najeriya masu ritaya ta sanar da...

Malami ya magantu kan sukar rashawa a mulkin marigayi Buhari

Tsohon babban Lauyan Najeriya kuma ministan shari'a, Abubakar Malami,...

Turkiyya ta gargadi Najeriya kan ‘yan ta’addar FETO

Gwamnatin Turkiyya ta fitar da wani gargadin cewa, mambobin...

Kiristoci sun jinjinawa Musulmai yadda aka yi jana’izar Buhari ba kashe kudi

Ana samun karuwar al’ummar Kudancin Najeriya musamman mabiya addinin...
X whatsapp