fidelitybank

Ba za mu yarda mu mutu a cikin PDP ba shi yasa muka koma APC – Sanatoci

Date:

Sanatocin Najeriya uku da suka fito daga jihar Kebbi, waɗanda suka sauya sheƙa daga babbar jam’iyyar adawa ta PDP zuwa APC mai mulki sun ce, sun fita daga jam’iyyar ce sanadiyyar rikice-rikice na cikin gida.

A jiya Talata ne shugabancin majalisar dattajai ya tabbatar da sauya shekar sanatocin wato Sanata Adamu Aliero mai wakiltar Kebbi ta tsakiya da Yahaya Abdullahi mai wakilartar Kebbi arewa da kuma Garba Maidoki mai wakiltar Kebbi ta kudu.

Sanatocin sun ce sun fice daga jam’iyyar ne saboda rikice rikicen cikin gida da suka yi wa jam’iyyar PDP katutu.

Daya daga cikinsu, Sanata Yahaya Abdullahi ya shaida wa BBC cewa a bayyane take tun bayan zaɓen 2023, jam’iyyar PDP ta shiga ruɗani da rikici kala-kala, kuma har kawo yanzu babu alamun jam’iyyar tana ɗaukar matakin gyara matsalolin nata.

Ya ce ”Kowa ya san dai abubuwan da suka addabi PDP, tana son ta wargaje. Ba kuwa wanda ke son ya shigo mu’amula da jama’a sai ka ga waɗanda ka zo kana son ka zauna da su kana tsammanin za a haɗa kai a ceto al’umma a gyara ƙasa, sai kansu duk ya rarrabu, abu ya ƙi ci, ya ƙi cinyewa kullum sai ƙara lalacewa ya ke.”

Ya yi bayanin cewa ai dama can da su aka kafa APC amma sun fice daga cikin ta ne saboda gwamnan su na wancan lokacin ya nuna baya yi da su, kuma sai PDP ta janye su, amma a yanzu yanayin ya canza domin kuwa asalin ƴan PDP su gaza ɗinke ɓarakar su ta cikin gida kuma ga shi a ”shugaban ƙasa Tinubu ya san amfanin mu, kuma shi sabon gwamna Dr Nasiru Idris Kauran Gwandu ƙaninmu ne, ya bamu girma ya bamu mutumcin mu, don haka irin wannan a kan me za mu zauna muna jayayya da shi.”

Sanata Yahaya Abdullahi ya kuma musanta cewa akwai alƙawarin da shugaba Tinuu ya yi masu, wanda ya sa suka sauya sheka zuwa APC inda ya ce shi a yanzu babu abin da bai gani ba a rayuwa domin haka ya wuce a yi mashi alƙawari kafin sauya sheƙa.

nnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp