Firamistan Isra’ila Benjamin Netanyahu, ya yi watsi da kiran dakatar da wuta tsakaninsa da Hamas.
Mista Netanyahu ya nanata cewa zai amince da tsagaita wuta na wucin gadi a matsayin musaya idan Hamas ta sako dukkan Isra’ilawan da ta ke yi garkuwa da su.
Ya ce ”mutane da dama a duniya sun yi kiran kar mu shiga Gaza, amma mun shiga. Sun ce kar mu shiga birnin Gaza, nan ma mun shiga, sun ce kar mu shiga Al-Shifa nan ma mun shiga. Dan haka babu batun tsagaita wutar dindindin sai dai ta wucin gadi”
Sai dai jaridar Washington Post, ta rawaito Isra’ila da Hamas da Amurka na gab da cimma matsayar sako mata da yaran.