Gwamnatin jihar Katsina ta musanta batun cewa, ta fara shiga sasanci da ƴanbindigar jihar, inda ta ce lallai babu hannunta a wannan batu.
Gwmanatin ta bayyana haka ne bayan wasu jagororin ƴanbindiga sun miƙa bindigogi da mutanen da suka yi garkuwa da su ga sojoji a jihar.
A wata tattaunawa da ya yi da Daily Trust, kwamishinan watsa labarai na jihar Katsina, Dr Bala Salisu ya ce gwamnatin jihar na kan bakarta cewa ba za su yi sulhu da ƴanbindiga ba.
Sai dai ya ce a shirye suke su karɓi duk wani ɗanbindigar da ya tuba da kansa, ya miƙa wuya.
A jiya ne rundunar sojin Najeriya ta ruwaito cewa wasu manyan ƴanbindiga sun miƙa bindigogi da mutanen da suka yi garkuwa da su ga sojoji a jihar ta Katsina.