Dakarun Ukraine na ci gaba da jajircewa, domin tabbatar da sojin Rasha ba su kutsa birnin Kyiv ba.
Sojin Ukraine sun haka ramuka masu zurfi da min kewaye mashigar Kyiv, yayin da wasu kuma suka kafa shingaye a kan hanya dauke da makaman roka da tankokin yaki.
Magajin birnin Kyiv Vitaliy Klitschko, ya ce, ba za su taba mika wuya ba.
Ya ce “a yanzu an ci gaba da gwabza yaki a Irpin da Bucha, da Hostomel, dakarunmu na fafatawa, abin da nake son shaida muku shi ne, babu inda za mu, ba kuma za mu bar Kyiv b, babu mai son mutuwa, amma dole mu tsaya mu kare ‘ya’yanmu da iyalanmu.”
Burinsu mu mika wuya, hakan kuwa ba za ta taba faruwa ba.