fidelitybank

Ba za mu taɓa yarda Lauyoyin Birtaniya su yi aiki a Najeriya ba – NBA

Date:

Shugaban ƙungiyar lauyoyin ta ƙasa NBA, Yakubu Maikyau, ya ce kungiyar ba za ta bari lauyoyin Burtaniya su yi aiki a Najeriya ba.

Wannan dai na da nasaba da rattaba hannun da ake zargin gwamnatin Najeriya da Birtaniya suka yi a kan yarjejeniyar kasuwanci da zuba jari ta ETIP.

Gidan talbijin na Channels ya rawaito cewa babban lauyan ya bayyana cewa an sanya hannu kan yarjejeniyar ba tare da amincewar NBA ba, yana mai cewa kungiyar za ta ci gaba da adawa da duk wata yarjejeniya da za ta kawo cikas ga dokar ƙasar.

“Wane ƙoƙari ne gwamnatin Najeriya ta yi don ganin lauyoyin Najeriya sun sami damar yin amfani da yanayin doka a Birtaniya? Abin da ya fi ban takaici shi ne yadda aka kulla yarjejeniyar ba tare da shigar da ƙungiyar lauyoyin ƙasar kan rubutun yarjejeniyar ba,” inji shi.

Maikyau ya kuma buƙaci shugaban kasa Bola Tinubu da ya kafa dokar ta-baci a cikin tabarbarewar tsaro da ya addabi kasar.

Yayin da yake kira ga Gwamnatin Tarayya da ta dauki kwararan matakai na magance matsalar rashin tsaro, Maikyau ya ba da shawarar saka hannun jari ga jami’an tsaro a kasar.

legit.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp