Firaministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi ne ta daƙile barazana biyu daga gwamnatin Iran – barazanar makaman nukiliya da ta manyan makamai masu linzami, kuma ya ce Isra’ila ta cimma burinta.
Ya ce Isra’ila ba za ta taba barin Iran ta samu ƙarfin ƙera makamai masu linzami 20,000 ba, ”saboda haka muka dauki matakin lalata fasaha da ƙarfinsu, kuma wannan shi ne abin da rundunar sojin Isra’ila ke yi a yanzu,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa: ”Mun bude hanyar shiga Tehran. Nan gaba kadan za ku ga jiragen yaƙin Isra’ila, da sojojin sama na Isra’ila, da matuka jiragenmu, a sararin samaniyar Tehran.”
Netanyahu ya ce Isra’ila za ta kai wa Iran hari a duk inda ta nufa, bayan da Iran din ta mayar da martani kan harin da Isra’ilar ta kai mata ranar Juma’a.
Iran ta harba makamai masu linzami cikin sassan biranen Isra’ila a jiya dadaddare, inda hukumomin Isra’ilar suka ce harin ya kashe mutum uku.