fidelitybank

Ba za mu kori Arteta ba duk da an fitar da mu – Arsenal

Date:

Arsenal ta cimma matsaya kan makomar Mikel Arteta a filin wasa na Emirates bayan ficewar Gunners daga gasar zakarun Turai.

Daily Mail, ta hanyar SPORTbible, ta ba da rahoton cewa shugabannin Gunners ba za su kori Arteta ba duk da rashin nasarar da kungiyar ta yi.

Mikel Arteta ya kalli kungiyarsa yayin da suka tashi 2-1 a hannun PSG a filin Parc des Princes ranar Laraba kuma sun tashi 3-1.

Sun yi tattaki zuwa babban birnin kasar Faransa da fatan za su juyar da rashin nasara da ci 1-0 a wasan farko, amma mafarki ne kawai.

Kwallaye da Fabian Ruiz (27′′) da Achraf Hakimi (72′) suka ci suka sanya ‘yan wasan na Paris cikin kwanciyar hankali kafin Bukayo Saka ya farke wa ƙungiyarsa kwallo a ƙarshen wasan (76′).

Sakamakon wasan na nufin Gunners za ta kawo karshen kakar wasa ba tare da wani kofi ba.

Tuni dai Arsenal ta sha kashi a hannun Liverpool a gasar Premier ta Ingila.

Arteta ya koma Gunners ne a shekarar 2019 amma bai samu damar jagorantar su zuwa ga manyan kayan azurfa ba tun kakar 2019-20 lokacin da suka doke Chelsea da ci 2-1 don daukar kofin FA.

Tun daga wannan lokacin Gunners ta lashe Community Shield guda biyu, amma ta kasa samun nasara a gasar.

Daily Mail ta rawaito cewa hukumar kulab din ba ta da shirin korar dan wasan na Spaniya nan ba da jimawa ba.

Ya kashe sama da fam miliyan 600 kan ‘yan wasa ciki har da fam miliyan 105 na sayen Declan Rice.

nnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar Æ´an Æ™asarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan ÆŠaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp